Saturday, February 15, 2025

ME ZA KU CE WA ALLAH? - Hausa Haiku 36 (Mai Carbi)

...daga alk'alamin Muhammad Tajajjini d'an Tijjani 1. Dukkan godiya ta tabbata gare Ka da kyautar Ka. 2. Na adabi da Ka ba mu ba tare da mun biya kwabo ba. 3. Wasu na zube wasu rubutun wak'e mu kwa Haikawa. 4. Ga wani zance da aka zanta a yau mai ban ta'ajib'. 5. "...Bi ni'imati Rabbika fa hadith" zan kawo gare ku. 6. Zan fara ne da wata fahimta da na gano ku gane. 7. Duk abin da ban samu ba, Allah ne bai ba ni ba. Haqqun. 8. Haka zalika wanda na samu, Allah ne ba kowa ba. 9. Wani ne ya ce yana da tambaya. A ka ce ana ji. 10. "Shin wai ku me za ku cewa Allah ne?" Sai kowa ya yi tsit. 11. Aka fad'a kogin tunani. Can sai wani ya ce "Godiya." 12. Don wAllah Azim dukkan wata ni'ima da d'an Adam zai... 13. Nema kuma ya ke fafutukar samu a doron k'asa? 14. Allah (SWT) Ya ba ni. Ba tawaya sai k'ari ma da Yai mana. 15. Allah Ya ba mu rai Ya ba mu lafiya. Ya ba mu ji ras. 16. Ya ba mu gani. Ya ba mu shinshina. Ga d'and'anonmu rau. 17. Sannan Ya ba mu fatar sanin yanayi har da hankali. 18. Allah Ya ba mu tunani.Ya ba mu ci da shan halali. 19. Ya halicce mu maza da mata Ya ba mu sura da tsari. 20. Yai mu Musulmi. Ya yardar mana bauta gare Shi Rabbi. ... 21. Ya ba mu iyaye Haihuwar mu halali. Ga sutura fes. 22. Ya ba mu mata da y'ay'a har jikoki tuli Ya ba mu. 23. Allah Ya ba mu muhalli da makwabta fal mãsu kirki. 24. Ga abin hawa natsuwa da wadatar zuci mun samu. 25. Har da arzik'i da kama kai. Ga aune da hangen nesa. 26. Allah Ya kai mu Makkah har da Madinah. Ya yardar mun... 27. Ziyarci Manzo (SAWS). Sallah a Haramainin nan masu tsarki. 28. Da naSa (AWJ) da na Nabiyyina Muhammad (SAWS) cikin harami. 29. Ya ba ni harshe mai ambaton Sa. Mai go- diya gare Shi. 30. Ala kulli hal Ya gudanar da ni kan tafarki mai kyau. 31. Allah Ya yardar mun shiga y'an Sittuna au Saba'una. 32. Mun shigo da kwarjini da kamala muna hamdala. 33. Sai tsawon rai mu wanye dunya lafiya Shi ne ya saura. 34. Ya Allah Ka ba mu sabur da juriya har can kushewa. 35. Abin da muke bid'a ke nan Ka sa mu cika da iman'. 36. Ka sa mu a Y'an radiyatan mardiyyah. Makur6an Kawthar." Amin thumma amin. (c)2025 Tijjani M. M. A Kiyayi Hak'k'in Mallaka

DUNIYA Y'AR YAYI - K'umbula 21

...daga alk'alamin Muhammad Tajajjini d'an Tijjani 1. Idan da akwai wani abu mai tabbas da ke d'orewa... 2. A doron k'asa ba zai wuce gushewar abin yayi ba. 3. In ana yayin abu wAllah kai ka ce ba zai kauce ba. 4. Ba zai ta6e ba! Amma a kwan a tashi sai ka ji shi d'if. 5. Gaba d'aya ka daina jin d'uriyarsa. Kamar ba ai ba. 6. Kai ko ambato balle labarinsa duk an daina yi kaf. 7. Duniya ke nan. Mutum an yi yayinka ma ya ka k'are... 8. Balle a ce ba ai ba. Kowa duniya ta rungume shi 9. Sai ya makance. Ya kama ganin shi fa na musamman ne. 10. Na baya ne ba su iya ba, shi ya sa ta rufta da su. 11. Ta shi ba irin ta su ba ce! Da sannu kowa zai gane. 12. Amma ina! Can sai ka ga mai hawa Jeep na sayan yalo. 13. Yana k'orafin an mas tsadar ta hamsin. Ko kunya bai ji. 14. An daina cin su Shawarma da shan Laban an koma koko. 15. Takalmin rafta rigar jeme ba wanki. Fuska a kod'e. 16. Da ba a Sallah don ba lokaci, yanzu ko ba natsuwa. 17. Su na ji su na gani ana biki ba zanin d'aurawa. 18. Jiya ta tafi da shurarsu, ta bar su k'anzon zubarwa. 19. K'uncin yau daban na gobe wa ya san ko za ta iso mas? 20. Don kewar tashe kan kashe bawa ko da bai mace ba. 21. Ka gan shi iska na kad'awa a gari ganye a bushe. ©2025 Tijjani M. M. A Kiyayi Haƙƙin Mallaka

K'UMBULA (Hausa Haiku) TA FARKO - Mai Carbi 40

...daga Alƙalamin Muhammad Tajajjini d'an Tijjani 1. Komai kyawun y’a Dole uba ya bayar Ko ta zam kwantai! (c)2017 tijjani m.m. 2. Wannan shi ne Haikun Hausa na farko da na rubuta. 3. A shekara ta Dubu biyu da goma sha bakwai cifcif. 4. Ta sanadiyar rubuta wasu Haiku na Turanci ne… 5. Akan iyaye masu shagwaɓa y'ay'a har su k'i aure. 6. Kwatsam! Kai ka ce walkiya baitin ya duro mun a ka. 7. Nan take na yi sauri na rubuta shi ba k'ak'k'autawa. 9. Daga nan fa na kama rubuta wasu. Kun ji mafari. 10. Wani ne ya ce in kawo K'umbala ta farkon ƙyanƙyasa. 11. Ya kuma ce mun yaushe a ka yi haka? Ta wane dalil'? 12. Shi ne na shiga rumbun ajiyata na kama lalube. 13. Duba nan duba can har soshal midiya ban same ta ba. 14. Nan na zurfafa bincike, ko'ina d'if. Na buga Haiku… 15. A manhajar "Search Machine" na Google don su taya ni nema. 16. Aka ba ni su fiye da milyan ɗari. Nan na yi turus. 17. Na canja zuwa Hausa Haiku. Nan ma La! Na ce "Wai! To fa!" 18. Can zuciyata ta ce da ni "Ka nemi natsuwa malam." 19. Na shiga kogin tunani "To a ina kwa zan samo ta?" 20. Kwana na wajen bakwai a nema. Da kyar na samo wAllah. 21. Ita kak'ai tilo a cikin wak'ok'i tuli a na'urata. 22. Kun san da farko tsoron a ganta ma na dinga ji. E. 23. To abu ne da ba a san shi balle a ce an yi sabo. 24. Kuma na san za a sha fama ka6ar ta. In ma an kar6a. 25. Can nai ta maza na gabatar da ita a tararrabe. 26. Dare ya tsala a shekarar Korona sahu ya d'auke. 27. Ai kuwa gari na wayewa wasu su ka ce "Atafau!" 28. Aka kama karaf- kiya. Masu "Ba ma so ba ma yi" na yi. 29. Haka rayuwa ta gada. Kuma hali ne na d'an Adam 30. Ko mene ne a ka ce sabo ne kar'ba sai a hankali. 31. Tarihi abu ne mai maimaita kansa. Yanzu komai ras. 32. Ba mu da abin cewa sai Hamd'lillah. Hak'uri ya yi. 33. Har sunan yanka Manya suka rad'awa Haiku na Hausa. 34. Ga shi mun samu har an soma rubuta Ajaminta yau. 35. Masana wasu sun fara kallonta don su nazarce ta. 36. Ko a tilonta ko ka ja carbinta K'umbula ta ke. 37. Haikawa mu ke masu k'aunar rubuta ta da harshenmu. 38. Bahaike ya ke ko Bahaikiya mace masoya Haiku. 39. Salon magana ne a adabi’ance Haiku da Hausa. 40. Kumbula ta ke y'ar kad'an mai albarka. Ma sha Allahu. *(c)2025 Tijjani M. M.* A Kiyayi Haƙƙin Mallaka

INCOMPLETE UNIVERSE - Poetry

...by Poetic Tee "Here take a sip." Why does it always, always makes me sad, makes my eyes go moist. Bringing tears to my ken, as my heart dip in reflection, making me realize how time, has flown by. Taking us with it, helplessly, like pieces of twigs, in a turbulence, a flooding river, emptying us, throu delta fingers, into a sea, further into an ocean. I don't even know which wAllaah. Yet, I know within my conscience, it's neither the Atlantic nor Pacific. Can't be! For our earth swims in it. Like a tiny speck of dust in another. Still in another bigger, vaster speck. All of them specks, upon specks, still upon a trillion other specks much more spectacular. Which makes me wonder, yes ponder, how small am I? Really! How much smaller still, in the vastness of the blackness, of this infinite, eternal space? Yes, I might be that nobody, that irrelevant, insignificant invisible atom. But surely, I am he unique, without which the universe will be incomplete? One of the many, off the periodic table, that bonds into a molecule, a compound, a complex system. That's thereafter gifted a soul, by the blown word "Kun!" And Lo! I become! A being! A human! A believer of The One. Unto Whom there's nothing like. This can't be real, right? O Livers in denial! Or can it? For here I am, floating in the stratosphere, hearing nothing, but listening to the sounds of silence, in absolute pitch darkness. My sight just like my shadow has totally abandoned me. No taste left in my mouth nor can I smell a thing. Numb, numb, numb with cold and voidness. A deja vous of sort. Like I once did in the womb, awaiting a birth and n soon a rebirth. An apocalypse. ©2024 Tijjani M. M. All Rights Reserved

DAMAMMIYAR FURA BA NONO BA SUGA - Waƙar Hausa

...daga alk'alamin Muhammad Tajajjini ɗan Tijjani An dad'e ana ruwa k'asa na shanyewa Komai duhun dare Gari na wayewa Duk mai ƙaunar Annabi Ba fa ya ta6ewa Komai bak'in cikin ɗd'antsako Ba zai suri d'an shirwa ba. Dubi hak'k'in talaka Y'an siyasa na sacewa Wayoyinmu na hannu 'Barayinsu na k'wacewa Karatun allo da na boko Da yawan muna kasawa Sakaiyar wani zaluncin wAllahi ba sai an je lahira ba. Rayuwa yanzu ta fa lalace Azzalumai da yawa ake bautawa. Har tutiya wasu ke yi Sun hau tafarkin nan na baud'ewa. Zina da abar gudu abar 6oyewa Yau ta zame wa wasu abar shanawa. To kowa ya kwan da sanin Tuwo sunansa Tuwo ba zai canja ba. Abin damuwa abin kaico Na tattare da wasu y'an Arewa. Rashin ilimi rashin kishi Ya sa kullum muna dad'a ta6ewa. Hassada, k'yashi da bak'in ciki Sun taru sun hana mu had'd'ewa. Yanzu ga shi ba a sa mu cikin wad'anda suka san ci gaba. An yi Boko Haram ga Kidnapping Har da Bandits masu kasshewa. An hana mu noma, in ma mun yi Ina albarkar abin da muke shukawa? Hutun jaki dank'are da litattafai Amfanin ilimi aiki da shi don wayewa. Rashin sani kan sa kaza kwanci Bisa dami ba ta tsattsaga ba. Da yawan mu fa tafiya Kawai muke babu mai dubawa. Ina muka dosa a al'umance? Da yawa fa babu masu tonawa. Mun zama tamkar makafin Dabbobi da babu mai nusarwa. Yanzu a wannan k'arnin na AI Ba za mu samu wani jagora ba? Tajajjini nake d'an Tijjani Kira na yo ko da mai amsawa? In na aiko sak'on da Turanci Da yawa mutane ba a ganewa. Shi ya sa na yo ta sigar wak'e Duk da shike ban da gogewa. Fura ce na damo ba kindirmo Ku lalubi gard'inta don ban sa mata suga ba. (c)2024 Tijjani M. M. A Kiyayi Haƙƙin Mallaka

TIKITIN SHIGA WUTA (Ƙumbula 21)

...daga alk'alamin Muhammad Tajajjini ɗan Tijjani 1. Da kuɗi ake siyan tikitin shiga wutar Jahannam. 2. Al-jannah kuwa kyauta ake shiga da rahamar Allah. 3. Ga wanda bai je gano kan karatun ba to matso ka ji. 4. Da kuɗi ake sayen giya ai tatil. A nemi mata. 5. A yi zinace- zinace har luwaɗi da ma yankan kai. 6. A sai wa boka buƙatunsa na shirka. Ai sharholiya. 7. Da baɗala da shaye-shaye ai mankas. Ai biyan kisa. 8. A nemi mulkin da akan yi maguɗi a ke zalunci. 9. Kan su ake ruf-da-ciki kan haƙƙin talakawa fa! 10. A sauyawa duk halittar Allah kama don ai yaudara. 11. A tauye mudu a zambaci bayi su rasa mafita. 12. Ga abubuwa nan birjik da ake yi na zaluntar kai. 13. Wanda in mutum ya mutu yana yin su to wuta balbal! 14. Amma Al-Jannah fa? Ko kwabo ba za ka kashe ba wAllah. 15. Illa kawai kai alwala ka yi Sallah. Ka ba da Zakkah 16. Ka yi Azumi ka je Hajji kai Zikir. Ka nemi gafar'. 17. Ku duba da kyau a waɗannan tafarkin wanne ne aibu? 18. Ka kula da kyau duk rintsi kar ka mutu ba ka da Iman. 19. In ka yi sa'a Shahada ta zam kalma ta karshen harshe. 20. To yanzu ka ji azancin maganar da nai kan tijarar. 21. Kukan kurciya jawabi, mai hankali ke zama wayis. (c)2025 Tijjani M. M. A Kiyayi Haƙƙin Mallaka

HANA BAƊALA A SOSHAL MIDIYA AIKIN KOWA NE - Hausa Haiku

...daga alƙalamin Muhammad Tajajjini ɗan Tijjani 1. Yau dai wAllahi na ga abin da ya ban mamaki kwarai. 2. Wani gardi na gani na cin na jaki! Bulalu shaaraaaf! 3. Yana ihu a na ku ƙara mas dubu gobe ya sake. 4. Duk wanda bai da mafaɗi bai ji daɗi ba sam wAllahi. 5. A ce yaro ya doshi faɗawa wuta bai da makwaɓi. 6. Bai da uwa ta gari da za ta yi wuf ta sure ɗanta. 7. Ta sa ido ta hana cuta atafau ta cutar da shi. 8. Dakarun gidan mahaifin Y. Amurka sun kyauta wAllah!. 9. Da suka zane shi ciki da bai har ma da ɗoriya. 10. Suka kaddamar da bulalar hana shi baɗalar Tiktok. 11. Da iyaye da ahli na yin haka ai da anga gyara. 12. Da irin su O' da duk sun daina rashin "M" a dandali. 13. Saboda neman kuɗi maras tsafta sai mutum ya kife. 14. Shi ko ko oho. Kima da martabar gidansu a tir. 15. Yanzu da Hizbah ce ta hora shi ka ji tarantsin banza! 16. To hanin munkar aiki ne akan kowa! in Musulmi ne. 18. Da hannu da baki da zuci ga mai raunin imani. 19. Amma ai shiru wAllah ba daidai ba ne. Dole a motsa. 20. Wani lokaci magana ba ta isa sai da dorina! 21. Haka Allaah Yai umarni a Qur'ani. A sharɓa musu! *©2025 Tijjani M. M.* A Kiyayi Haƙƙin Mallaka

HAUSA HAIKU BA A YIN KA DA WARGI

...daga alk'alamin Muhammad Tajajjini d'an Tijjani 1. Haiku fa na da dokoki da ka'idar ga66ai a k'irge. 2. Komai na shi da lissafi yake tafe. Haiku sai mai Mas. 3. Duk wanda bai da rumbun kalmomi to na shi yai kallo. 4. Dalili shi ne nemawa kalma gurbi da ma madadi. 5. Don Hausa Haiku sai fasihi na gaske ke rubuta shi. 6. Ban da ma'ana ta kalmar akwai wasu buk'atu daban. 7. Wanda dole ne su tabbata in har da gaske za a yi. 8. In kuwa zance kawai za ai to akwai adabin zube. 9. Rarara kowa yai. Amma kun ga ana Haiku da wargi? 10. wAllah ko gwanin rubutacciyar wak'a ko ko marera. 11. Ba su tunkarar Haiku da Hausa gaba gad'i. Sam! Inaa! 12. Shi ba a rera shi balle a nemi sai an k'afiye shi. 13. Su 'Dango su 'Kwar duk ajje su. Samu kalma ta dace. 14. Ga66anta kar su zarce kirgen bulo a gina baitinka. 15. Ban da d'aukar kalma a ya6a. Lallai ne sai ka k'irga. 16. Hausa Haiku sam ba fili ba ne awon igiya. Lala! 17. Awon Gwamnati ne da duk takardunsa har Satifiket. 18. Shi ya sa Haiku da Hausa sai gwanayen jera kalmomi. 19. Da ga6obi sha bakwai cifcif kan sahu uku bi da bi. 20. Ga6o6i biyar sama, bakwai a tsaka biyar a k'asa. 21. Sannan a nemi ma'ana don kowa ya gane sak'onka. (c)2025 Tijjani M. M. A Kiyayi Haƙƙin Mallaka

EACH STEP, A DAY - Poetry

...by Poetic Tee "Here, take a sip." My journey, is back to You From whence and where It all began, not so long ago. Every day, like a step I take, Brings me closer back home Soon, this sojourn 'll be over. Tests, trials, travails on a trail Some I succeed, others I fail. As human, 9 I'm, never 'll be 10. Hope, fills me up to the brim In expectation, yes anticipation I'll walk into a graceful mercy. A thunderous welcome it is. Not worthy of the ungrateful But of Your Promise, fulfilled. (c)2025 Tijjani M. M. All Rights Reserved

FAILURES ARE STEPPING STONE TO SUCCESS

Then WASC/WAEC were really a test of the best brains. Getting straight As in 8 subjects was an achievement for the likes of Ahmad Sarkis, one in a century. Some of the brilliant minds would barely manage to scrape in 5 or 6 credits with P7 or two passes. Most end up with 2 - 4 credits and the rest will be passes. Such persons will still get admission in the university to read courses they never planned to have in their cap feathers. Those who insist on reading a course they desire, such as I, would go for remedials. However, like Prof. Abdalla Uba Adamu pointed out, guys like him found their rhymes and rhythms, eventually hitting their peaks and coming out on top of their classes, carting home awards, job offers and even scholarships to study abroad. I was one of them. Unlike now, where a student will pass out of secondary school with 8 or 9As only to end up at the middle or lower end of a table at a university of his or her choice. Lecturers use to be amazed. That was when they discovered such students results were often fake Matters got worse when NECO came on board as an examination body. Students with As and Bs in all subjects would find it difficult to gain admission into universities, repeat JAMB 5 or 6 times and still fail, and get frustrated out of their academic pursuits. So sad. And soon what eventually came to pass? Parents started sending their wards to get educated abroad due to persistent strike actions by ASUU which often prolong a 3-4 years course to 5-6 years before graduation and NYSC. Anyways, all that is history now. Many get a degree or 2 or even 3 and because they are never prepared to use the knowledge they acquire as a base upon which to use and become self employed and eventual employers of labour, non-graduates now fair better. Like our elders would say, there's nothing wrong with a child falling down. All he needs do is get up, dust off the dirt and continue to walk or run to his destination. If however the child fail to get off the ground and move on, then something is terribly, definitely amiss. So, worry not about failure or missing out on an opportunity. A better ootion is coming your way, that's why you missed the first one or a lesson is being taught to you, experience is being added to your personal development pool to make you a better goal getter.

Wednesday, February 12, 2025

MATTERS NOT WHO COMES FIRST OR LAST

I discovered that a long time ago wAllahi. That winning 1st Position in class is nothing special. How did I find that out? Well, while in Primary 4 promotional exams, 2 of my subject results were mistakely omitted from my Report Card by our teacher. So I ended up at the 5th position overall. I cried foul and filed a complain. The papers were checked and it was discovered I was truly on top of the class. So the guys positioned 1st - 4th were to each be moved off those positions down to accommodate my worthy 1st position. Then it occurred to me, why bother? What would it change, after all I've not failed and everybody knew I topped the class. Besides those not in our class knew nothing about the miscarriage. Why strip my classmates of the joy of their then celebrated positions. Kawai sai na ce a bar shi ba komai. Everybody was pleased with my decision, I inclusive. Since then it never mattered to me who's 1st, 2nd, 3rd or whatever. All i cared about is not failing. And it sufficed, becoming one of my cardinal guiding principles in life. So now I don't care who's where or doing what. I'm often contented with where I am and doing what I am doing. Whoever is doing whatever, his or her luck. Just let me do my own thing. I'm not competing with nobody wAllahi. And life has been very fulfilling for me. Ma sha Allah. Alhamdulillah. I often tell myself that all i wish for from Allaah SWT is finding myself among the list of those who made it to Jannah. Whether it's Adn, Firdous, Na'im, Ma'awa etc it doesn't really matter. So long as it's not Jahannam, I'm good, happy and pleased with my Lord, knowing He has gifted me the ultimate of successes. To same with hayatad dunya. Ni dai kawai kar in yi failing. No failure please. That's all.