THIS IS A "DISCOVERY BLOG", JUST LIKE THE HEAVENS* WITH IT I SET MY MIND FREEEEEEEEEEEE...* YOU ARE WELCOME TO SHARE MY WORLD (both the physical and abstract)* So do come again and again...
Saturday, February 15, 2025
TIKITIN SHIGA WUTA (Ƙumbula 21)
...daga alk'alamin Muhammad Tajajjini ɗan Tijjani
1.
Da kuɗi ake
siyan tikitin shiga
wutar Jahannam.
2.
Al-jannah kuwa
kyauta ake shiga da
rahamar Allah.
3.
Ga wanda bai je
gano kan karatun ba
to matso ka ji.
4.
Da kuɗi ake
sayen giya ai tatil.
A nemi mata.
5.
A yi zinace-
zinace har luwaɗi
da ma yankan kai.
6.
A sai wa boka
buƙatunsa na shirka.
Ai sharholiya.
7.
Da baɗala da
shaye-shaye ai mankas.
Ai biyan kisa.
8.
A nemi mulkin
da akan yi maguɗi
a ke zalunci.
9.
Kan su ake
ruf-da-ciki kan haƙƙin
talakawa fa!
10.
A sauyawa duk
halittar Allah kama
don ai yaudara.
11.
A tauye mudu
a zambaci bayi su
rasa mafita.
12.
Ga abubuwa
nan birjik da ake yi
na zaluntar kai.
13.
Wanda in mutum
ya mutu yana yin su
to wuta balbal!
14.
Amma Al-Jannah
fa? Ko kwabo ba za ka
kashe ba wAllah.
15.
Illa kawai kai
alwala ka yi Sallah.
Ka ba da Zakkah
16.
Ka yi Azumi
ka je Hajji kai Zikir.
Ka nemi gafar'.
17.
Ku duba da kyau
a waɗannan tafarkin
wanne ne aibu?
18.
Ka kula da kyau
duk rintsi kar ka mutu
ba ka da Iman.
19.
In ka yi sa'a
Shahada ta zam kalma
ta karshen harshe.
20.
To yanzu ka ji
azancin maganar da
nai kan tijarar.
21.
Kukan kurciya
jawabi, mai hankali
ke zama wayis.
(c)2025 Tijjani M. M.
A Kiyayi Haƙƙin Mallaka
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
No comments:
Post a Comment