Monday, April 3, 2017

ACE MAIGIDA YA RABU DA BERAYEN DA KE GIDANSA...

... YA MAI DA HANKALI KAN NEMO ABINCIN DA MUTAN GIDAN ZA SU CI KAWAI? ANYA KUWA DA DUBARA A WANNAN LAMARIN?
~ Tijjani Muhammad Musa
Ka na nema ana fasa buhunan abincin ana kwashewa, ana sacewa, ana arcewa, ana neman ka ci gaba da sahalewa ka na kyalewa.
Toh, ai berayin ba su gudu ba. Da babansu da sauran berayen, su na nan a gidanka daram. Kuma ka dana tarkuna ka na kama su, amma wasu na sa hannu su na kwanche su, sannan su sake su a cikin gidan na ka.
Sannan berayen ba su bar aniyarsu ba. Ka na kaffa-kaffa da abinda ka ke samu, su na yi maka aringizon huqatarsu don su cutar da kai da ahlinka. Ka yi jinkirin tabbatar da abubuwan da za ka gudanar, amma mutan gidanka saboda rashin sani, sun yi caa su na kukan ba ka son ci gabansu.
Sannan ka na kama berayen, karnukan farautarsu na haushi su na hana ka samun abinda za ka gudanar da alkawarin da ka yi wa mutanen gidan na ka ta hanyar 6ula ma ka buhunan hatsinka da fasa maka bututur ruwa. Makiyi ba kyau. Ga 6arna, ga 6arnatarwa.
Su na iqirarin su ma su kishin gidanka ne, amma fa nufinsu ala kulli halin su ga kifewarka. Buqatarsu cewa ko dai ka saki berayen da ka kama, su sakata su wataya yadda su ke so, ko su daqile babbar hanyar samun dukanin arziqin da ka ke nema don ciyar da kuma gina gidanka.
Banda fa sace-sacen da aka yi naka, ka na ganin kayan kurukuru an qi a dawo ma ka da su, don amfanin mutan gidanka. Sannan ga ci gaba da iskancin da ake yi tun ba ka nan don kawai sabo da yi, kuma a nuna ma ka ba ka isa ka hana ba.
Sannan duk iya kokarinka na gyara abubuwan da za su samawa mutan gidanka sauqir rayuwa, wadansu marasa kishin ci gaban gidan na ka su na cin dunduniyarka, su na yi ma ka batanci, su nai maka zagon kasa ta kowane fanni.
Amma don rashin ta ido, su na kira da ka rabu da barayin nan da abinda su ka satanma, wanda da shi su ke amfani su na lalata tafiyarka, su na hanaka gudanar da lamuran fidda jakinka daga duma. Burinsu ka gaza kai gaci, su ai dama duk kanwar jaa ce.
Ta yaya za ka ci gaba da wanzar da samun natsuwa ga mutanen gidanka, sannan ga koke da qorafe-qorafensu? Maimakon su dafa ma ka, su cicci6a ma ka, su kama ma ka, don a gudu tare, a tsira tare. Ina!!! Toshewar basira, su so su ke a bar berayen su ci karensu ba babbaka.
Abin ya na daure mun kai wAllaahi.

FESBUK NA NEMAN TAIMAKON HAUSAWA

... SU TAYA SU YIN FASSARA

A ci gaban kokarin Facebook Administrators wato ma su kula da gudanar da harkar sadawarwa a dandalin sada zumunta na Fesbuk, yanzu haka sun manna wata buqata a shafi na cewa jama'a su taimaka wajen taya su fassara dukkan nau'in bayanai a shafukansu da ke cikin harshen Turanci izuwa harshen Hausa don tabbatar da samarwa al'ummar Hausawa jin dadi da walwalar yin Fesbuk da Hausa.
Duk da shi ke da dai so samu ne da sai mu bukaci, su dauki mutanenmu da su ka karanci Hausa daga matakin digiri ko kwatankwacin sa izzuwa digirgir, kai harma ma su PhD wata Daktaa ke nan aiki don gudanar mu su da wannan bukata.
Ka ga ta hakan, mu ma na mu sai su samu kudin shiga, kuma da yawa za'a daina raina karanta Hausa a jami'oinmu. Don wasu gani su ke yi abin dariya ne a ce dalibi ya na karanta harshen mahaifiyar a matakin digiri a jami'a. Alhali kuwa ba ko kusa ba haka ba ne.
Toh, ni dai ga abinda su ka manna a saman shafina da na bude shi yanzu:
Help translate Facebook into Hausa
Keep the language of Facebook in authentic Hausa by translating and voting on translations.
Start now
Kun ga akwai buqatar mu tashi tsaye don tabbatar da wannan gatan da Allaah SWT Ya yi wa harshen Hausa, don mu dada shigar da shi cikin harsunan duniya da yanzu haka aka yarda da su, kuma ake amfani da su wajen sadarwa a kafafen yada labarai da gudanar da harkoki a duniya.
Mu dai in sha Allaahu za mu bada ta mu gudummawar.
TMM

ALBISHIRINKU? KU CE GORO! FARI TAS!!!


Kuma ace Harshen Hausa bai yi fice ba?

Yanzu haka dai ma su Facebook sun soma bada za6in yin harkokin ma su amfani da dandalin sada zumuntarsu a cikin harshen Hausa kamar yadda sauran kafafen yada labarai irin su Sashen Hausa na BBC, Muryar Amurka (VOA), Muryar Jama'ar Jamus (DW), Radio Faransa (RFI), Radio Chaina da dai sauransu su ke yi tun fil-azum.
Gani na yi an jero Hausa cikin jerin gwanon harsunan duniya daban-daban kamar su Turanci, Faransanci, Jamusanci, Larabci, Sufaniaci da dai makamantansu ana nuna mun ko ina son in gudanar da al'amurana a dandalin Facebook cikin harshen uwata, wato Hausa?
Abun kamar almara, ina latsa zabin Hausa, sai komai ya kamar rikidewa, rubutunsu daga kamfaanin Facebook duk su ka jujjuya izuwa harufan Hausa. Na ce "Kai! WAllahi da gaske ne!"
Sai dai fa kar ku shagala, dukkan wanda ya yi rubutunsa cikin harshen Turanci ko Larabci, toh babu fassararsu. A yadda mutane daga ko ina a duniya su ka yi rubutunsu, haka zai zo ma ka batare da na'urorin Facebook sun fassara ma ka rubutun ma'abota amfani da dandalinsu ba.
Wa ya isa ya yi Malam Bahaushe wannan gatan in ba Allaah ba?
Tuni mu ka riga mu ka ce a koma amfani da harshen Hausa wajen koyar da dalibanmu a makarantunmu kama daga Firamare har izuwa Jami'a.

Kuma kuskuren da Aisha Buhari ta yi ke nan da ta kai ziyara kasar Amurka stin da ya gabata. Da kawai ta yi jawabinta da harshen Hausa a United State Institute of Peace (USIP) a can birnin Washington DC, da ba'a yi mata dariyar bata iya Turanci ba.
In ya so ta bar su da neman kwararru, ma su iya fassara daga Hausa izuwa dukkan sauran Harsuna duniya ta yi tahowarta gida kawai. Ai kuwa kunga da ta dora damba, kuma ta kafa tarihin da duniya ba za'a taba mantawa da ita ba.
Ta haka ma da sai ta kwaci al'ummarta daga wannan qangin yin amfani da harshen wadanda su ka yi mana mulkin mallaka wato turawa ke nan. Amma dai ba ji. Ai ana tafe kan isa. Saura qiris haqanmu, mu ma su wannan kira kusan shekaru 20 baya, ya cimma ruwa.
Mu dai yanzu haka da Hausa mu ke yin Fesbukin wAllaahi. AlhamdulilLlah, Ma sha Allaah.

THE ALMAJIRI CHALLENGE

~ Tijjani Muhammad Musa
Image may contain: 1 person, standing and outdoorIf we are really serious and sincere about solving this Almajiri problem in Northern Nigeria, one of the sure ways is for each rich, well-to-do, elite or middle-class man with at least a degree, working, possibly married with a child or two to volunteer in sponsoring, just like we will our own children, you and I, the EDUCATION of at least ONE of the ALMAJIRIS roaming the street in our society, from PRIMARY to UNIVERSITY DEGREE LEVEL.
A promise should be extracted or agreed upon with the almajiri, child of the poor or ward of any neighbor being sponsored with consent of his parents or guardian, that if blessed with the education to degree level, he or she will be expected to similarly extend the same sponsorship opportunity to at least one less privileged child like him or her.

Based on this projection, it is envisaged that in the next 5-10 years, the low level of education and poor corporate and economic involvement of the average Northern Nigerian in state, national and international affairs would gradually start to decrease and eventually disappear from the populace. It is obvious, the problem will not abate just because we keep talking or complaining about it. We must take definitive action towards addressing it, in order to achieve our set objectives of eradicating the scourge known as the Almajiri Phenomenon.
But our coming on to social network platforms such as Facebook, Whatsapp, Twitter and so on to simply hype on it from the comfort of our homes, offices, play stations to show the world we are worried about it and expect the problem to simply vanish into thin air, will not work. Affirmative action must be taken by each of us towards eradicating the menace. We must change our attitudes, if we are to bring any meaningful progress in this regard.

SPONSOR THE EDUCATION OF AT LEAST ONE ALMAJIRI TO DEGREE LEVEL.

QALUBALE GA MA SU IQIRARIN MATSALAR ALMAJIRCI...



... A JIHOHINMU NA AREWACIN NAJERIYA YA DAME SU
~ Tijjani Muhammad Musa

Image may contain: one or more people
In dai da gaske mu ke, mu na son mu shawo kan wannan matsalar ta Almajirai a Arewancin Najeriya, toh dukkan wani mai arziki da wadata, ko mai ilimin boko aqalla matakin digiri na farko, kuma ma'aikaci, magidanci, mai yaro ko yara, ya qudiri niyyar daukan nauyin ilimintar da wani Almajiri ko yaro na 'yan uwa ko makwabta aqalla guda daya tun daga makarantar Firamare har sai shima ya kammala karatunsa na digirin farko a Jimi'a kamar yadda za mu yi wa 'ya'ya haifaffun cikinmu.
A qulla 'yarjejeniya da almajirin ko yaron da aka dauki nauyinsa ko ita, cewa in har Allaah Ya tabbatar masa/ta da samun wannan matsayi, wato na zama mai digiri a rayuwarsa/ta, toh shima ko itama za su nemi wani ko wata daga almajirai ko 'ya'yan talakawa ya/ta dau nauyin ilimantar da su har sai su ma sun mallaki kwalin digiri ko kwatankwacinsa,
Ta haka, akwai kyakkyawon hasashen cewa, nan da 'yan shekaru 5-10 wannan yanayi da Arewa ta ke ciki na koma bayan ilimi da rashin ci gaba zai dau tushen kaucewa daga al'ummarmu. Wasu dai tuni sun riga sun fara. Don kuwa matsalar ba za ta kau ba, don kawai anata cecekuce da koken da ake yi a baki kawai. Dole sai mutane sun dauki matakai na yin wani abu akai, sannan za'a samu cimma burin da aka sa a gaba.
Image may contain: 2 people, people standingAmma a zo dandalin sada zumunta na intanet, wato 'Social media' kowa ya na yamadidin abin na bashi kunya, ko ya dauki hoton almajiri ya na nunawa duniya cewa wai shi abin ya dame shi ba'a nan take ba. An dade ana ruwa, kasa na tsotsewa. Ya kamata mun canja salo kuma.
DAUKI NAUYIN ILIMANTAR DA ALMAJIRI GUDA DAYA!